Wadda Zai Gaje Ni Manomi ne..... Tsohon gwamna Badaru

Jigawa New Media Office
0
"Wadda Zai Gaje ni Manomi ne"

-Tsohon Gwamna Badaru

A yau kenan, bayan zagayen duba yadda ake gudanar da rabon kayan noman alkama karkashin shirin NAGS-AP na gwamnatin tarayya tare da hadin gwiwar gwamnatin jihar Jigawa...Mai girma gwamnan jihar  Mallam Umar A. Namadi FCA ya ke zagayen duba tasa gonar alkamar; domin ganin yadda aiki ke gudana.

 Akwai cibiyoyin rabon wannan kaya (Redemption center) da dama a faÉ—in jihar Jigawa musamman kananan hukumomi 22 da ake wannan shiri na bunÆ™asa aikin noman alkama a jihar Jigawa. Gwamnan ya ziyarci 6 daga cikin waÉ—annan cibiyoyin wadda su ka hada da Kiyawa, Jahun, Miga, Kafin Hausa, Auyo, Hadejia, Guri da Birniwa.

A zagayen  da mai girma gwamnan ya ke, ya gane wa idonsa yadda rabon ke gudana a wadannan cibiyoyi tare da sake jan kunnen wannan jami'ai wajen ganin an rabawa manoman a kan lokaci da kuma tabbatar da yin adalci.

Post a Comment

0Comments
Post a Comment (0)